RFI Hausa
banner
ha.rfi.fr
RFI Hausa
@ha.rfi.fr
🌍 Sashen Hausa na RFI na maraba da ku a shafin Bluesky
💻 rfi.fr/ha/ 🎧 rfi.my/kai-tsaye
𝕏 rfi.my/Xha 📷 rfi.my/IGha 🗨️ rfi.my/WAha
Sojojin Mali sun kashe jagoran JNIM da suka addabi ƙasar
Sojojin Mali sun kashe jagoran JNIM da suka addabi ƙasar
Rundunar sojin Mali ta tabbatar da kisan Abou Salam Oumarou, wanda shi ne shugaban ƙungiyar ƴan ta’adda ta JNIM da suka addabi ƙasar, a wani samame da ta gudanar a yankin Soumpi, kamar yadda majiyoyi da dama suka tabbatar.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 2:24 PM
Sojoji sun kuɓutar da ƴan bautar ƙasa 74 daga yiwuwar faɗawa hannun Boko Haram a Najeriya
Sojoji sun kuɓutar da ƴan bautar ƙasa 74 daga yiwuwar faɗawa hannun Boko Haram a Najeriya
Dakarun haɗin gwiwa na Operation Hadin Kai (JTF) sun ceto matasa ƴan bautar ƙasa 74 daga yuwuwar faɗawa hannun ƴan ta’addan Boko Haram/ISWAP a kan hanyar Buratai–Kamuya da ke jihar Borno.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 1:43 PM
An sami sassaucin ƙawanya da ƴan ta'adda suka yiwa birnin Bamako na Mali
An sami sassaucin ƙawanya da ƴan ta'adda suka yiwa birnin Bamako na Mali
Masu tayar da ƙayar baya a Mali, sun sassauta ƙawanyar da suka yi a garuruwan ƙasar, bayan makonni da aka ɗauka ƙasar na cikin mummunan tashin hankali, kasancewar birnin Bamako ne kaɗai ya kasance ƙarƙashin ikon gwamnati.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 1:16 PM
Sudan ta yi watsi da ƙungiyar Quartet da aka kafa don aikin maido da zaman lafiya a ƙasar
Sudan ta yi watsi da ƙungiyar Quartet da aka kafa don aikin maido da zaman lafiya a ƙasar
Gwamnatin Sudan ta bayyana adawa da ƙungiyar Quartet wadda ta ƙunshi Amurka, Hadaddiyar Daular Larabawa, Masar da Saudiyya wadda aka kafa domin samar da zaman lafiya a Sudan.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 1:03 PM
Musulmi ne hare-haren Boko Haram ya fi shafa a Najeriya ba Kiristoci ba - AU
Musulmi ne hare-haren Boko Haram ya fi shafa a Najeriya ba Kiristoci ba - AU
Shugaban ƙungiyar Tarayyar Afirka Mahamoud Ali Youssouf, ya ce babu wani abu mai kama da kisan kiyashi da mabiya addinin Kirista ke fuskanta, a yankin Arewacin Najeriya.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 9:54 AM
Najeriya ta dakatar da ƙarin harajin kashi 15 na man fetur da ake shigarwa ƙasar
Najeriya ta dakatar da ƙarin harajin kashi 15 na man fetur da ake shigarwa ƙasar
Hukumar Kula da Albarkatun Mai na Cikin Ruwa da kuma Kantudu ta Najeriya NMDPRA, ta sanar da dakatar da shirin fara amsar ƙarin haraji na kashi 15, kan man fetur da kuma gas da ake shigarwa ƙasar.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 9:13 AM
Ɗalibai a Najeriya sun yi maraba da dokar hukunta Malaman da ke cin zarafin mata
Ɗalibai a Najeriya sun yi maraba da dokar hukunta Malaman da ke cin zarafin mata
A Najeriya, wasu ƙungiyoyin ɗalibai sun fara ala-san-barka da matakin Majalisar dattawan ƙasar da ta amince da dokar ɗaurin shekara 14 ga duk wani malamin makarantar gaba da sakandare da aka samu da laifin cin zarafin dalibai.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 8:06 AM
Ƴan ƙwadago a Ghana sun yi watsi da tayin ƙarin kashi 9 na albashin ma'aikata
Ƴan ƙwadago a Ghana sun yi watsi da tayin ƙarin kashi 9 na albashin ma'aikata
Wasu Ƙungiyoyin Ƙwadagon malaman makarantu a ƙasar Ghana sun bayyana rashin jin daɗinsu dangane da ƙarin albashin kashi 9 cikin 100 da gwamnatin ƙasar ta sanar ga daukacin ma’aikatan da ke ƙarkashin albashin bai ɗaya waton Single Spine salary.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 8:06 AM
Tallafin kashi 44 cikin 100 ne kaɗai ke isa ga mabuƙata a Najeriya - Bankin Duniya
Tallafin kashi 44 cikin 100 ne kaɗai ke isa ga mabuƙata a Najeriya - Bankin Duniya
Bankin Duniya ya ce kaso 44 kacal ne cikin 100, na kuɗaɗen tallafawa al’umma ke shiga hannun mabukata a Najeriya, yayinda saura ke zirarewa.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 7:39 AM
Trump ya sanya hannu kan dokar da ta kawo ƙarshen katsewar ayyukan gwamnati
Trump ya sanya hannu kan dokar da ta kawo ƙarshen katsewar ayyukan gwamnati
Shugaba Amurka Donald Trump, ya rattaba hannu kan doka da ta kawo ƙarshen dakatar da ayyukan gwamnati mafi daɗewa a tarihin ƙasar, sa’oi kaɗan bayan da majalisar wakilan ƙasar tabi sahun ta dattijai kan wannan ƙudiri.
www.rfi.fr
November 13, 2025 at 6:58 AM
Amnesty ta gano ƴanbindiga da ke addabar mazauna Yankin Kudu Maso Gabashin Najeriya
Amnesty ta gano ƴanbindiga da ke addabar mazauna Yankin Kudu Maso Gabashin Najeriya
Ƙungiyar kare hakkin ɗan Adam ta Amnesty International a Najeriya, ta ce ta gano wasu gungun ƴanbindiga da ke addabar mazauna yankin Kudu maso Gabashin ƙasar.
www.rfi.fr
November 12, 2025 at 3:27 PM
Ana fargabar mutuwar baƙin haure 42 bayan kifewar jirginsu a tekun Libya
Ana fargabar mutuwar baƙin haure 42 bayan kifewar jirginsu a tekun Libya
Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da wasu alƙaluman da ke bayyana cewa baƙin haure 42 ne suka ɓace waɗanda yanzu haka ake kyautata zaton sun mutu, bayan da wani jirgin ruwan roba da ke ɗauke da su ya kife a gabar tekun Libya a makon da ya gabata.
www.rfi.fr
November 12, 2025 at 3:00 PM
Abu biyar da ya kamata ku sani game da taron G20 da zai gudana a Afirka ta Kudu
Abu biyar da ya kamata ku sani game da taron G20 da zai gudana a Afirka ta Kudu
Shugabannin ƙasashe masu tattalin arziƙi na G20 na shirin hallara a birnin Johannesburg na Afrika ta Kudu a ranar 22 zuwa 23 ga Nuwamba don halartar taron ƙungiyar wanda a karon farko ake gudanarwa a Nahiyar Afrika.
www.rfi.fr
November 12, 2025 at 2:46 PM
Sanwo-Olu ya buƙaci ƴan Najeriya su hada kai wajen shawo kan matsalolin ƙasar
Sanwo-Olu ya buƙaci ƴan Najeriya su hada kai wajen shawo kan matsalolin ƙasar
A yayin da a Ke ci gaba da cecekuce a kan barazanar da shugabaan Amurka Donald Trump ya yi a kan Najeriya, kungiyoyi da dama musamman yankin Arewacin kasar na ci gaba da gudanar da tarurruka domin fayyace gaskiya lamarin.
www.rfi.fr
November 12, 2025 at 9:22 AM
MDD ta yi tattaunawa kan batun isar kayayakin agaji a sassan Sudan
MDD ta yi tattaunawa kan batun isar kayayakin agaji a sassan Sudan
Shugaban hukumar ayyukan jinƙai na Malajisar Ɗinkin Duniya Tom Fletcher tare da hafsan sojojin Sudan Janar Abdel Fattah al-Burhan sun gudanar da taro na musamman, domin tabbatar da kayyakin jinkai sun isa sassan ƙasar da rikici ya ɗai-ɗaita.
www.rfi.fr
November 12, 2025 at 9:09 AM
Macron da Abbas sun kafa kwamitin tsara Kundin Tsarin Mulkin ƙasar Falasɗinu
Macron da Abbas sun kafa kwamitin tsara Kundin Tsarin Mulkin ƙasar Falasɗinu
Shugaban Faransa Emmanuel Macron da takwaransa na Yankin Falasɗinu Mahmoud Abbas, sun sanar da kafa kwamitin haɗin gwiwa da zai tsara daftarin Kundin Tsarin Mulkin ƙasar Falasɗinu.
www.rfi.fr
November 12, 2025 at 9:09 AM
Hare-haren ƴan bindiga sun tilastawa mazauna wasu yankunan Kano barin muhallansu
Hare-haren ƴan bindiga sun tilastawa mazauna wasu yankunan Kano barin muhallansu
Mazauna yankunan ƙananan hukumomin Tsanyawa da Shanono a jihar Kano da ke Arewacin Najeriya, na cigaba da ƙauracewa muhallan su sakamakon hare haren ƴan bindiga.
www.rfi.fr
November 12, 2025 at 8:55 AM
Sarkin Asante na Ghana ya yaba da mayar da kayan tarihi da Afirka ta Kudu da Birtaniya suka sace
Sarkin Asante na Ghana ya yaba da mayar da kayan tarihi da Afirka ta Kudu da Birtaniya suka sace
Sarkin Asante na Ghana, Otumfuo Osei Tutu na biyu, ya bayyana farin cikin sa, bayan da ƙasashen Burtaniya da Afrika ta Kudu ta mayar da wasu kayan tarihi 130 na zinariya da tagulla, waɗanda aka sace su a lokacin Mulkin Mallaka.
www.rfi.fr
November 11, 2025 at 6:04 PM
Dangote ya kulla yarjejeniyar samar da taki tan 16,940 kowacce rana a Najeriya
Dangote ya kulla yarjejeniyar samar da taki tan 16,940 kowacce rana a Najeriya
Katafaren kamfanin Dangote ya sanar da cewar bangaren sa dake samar da takin zamani ya haɗa kai da takwaransa na thyssenkrupp Uhde dake ƙasar Jamus, domin samar da tan 16,940 na takin yuriya a wasu sabbin cibiyoyin da zai samar guda hudu a Najeriya.
www.rfi.fr
November 11, 2025 at 5:51 PM
Akwai yuwuwar wani ɓangaren Gaza ya ci gaba da kasancewa ƙarƙashin ikon Isra'ila
Akwai yuwuwar wani ɓangaren Gaza ya ci gaba da kasancewa ƙarƙashin ikon Isra'ila
Bayanai daga majiyoyi ƙwarara na nuni da cewa akwai yiwuwar raba Gaza biyu, inda ɓangare guda zai ci gaba da zama a ƙarƙashin Isra’ila, lamarin da ka iya daƙile shirin zaman lafiyar da shugaba Trump ya gabatar a kan yankin.
www.rfi.fr
November 11, 2025 at 4:30 PM
An saki mutum 60 da aka kama yayin zanga-zangar da ta biyo bayan zaɓe a Kamaru
An saki mutum 60 da aka kama yayin zanga-zangar da ta biyo bayan zaɓe a Kamaru
Ministan cikin gida na Kamaru, Paul Atanga Nji, ya tabbatar da sakin mutane kusan 60 da aka kama a Ngaoundere sakamakon rikicin da ya ɓarke ranar 12 ga Oktoba, bayan zaɓen shugaban ƙasar mai cike da ce-ce-ku-ce da aka yi.
www.rfi.fr
November 11, 2025 at 4:30 PM
Taliban ta ɗauki alhakin harin da ya kashe mutum 12 a Pakistan
Taliban ta ɗauki alhakin harin da ya kashe mutum 12 a Pakistan
Ƙungiyar Taliban ta Pakistan ta ɗauki alhakin harin ƙunar baƙin wake wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 12 a babban birnin ƙasar Islamabad wannan Talata.
www.rfi.fr
November 11, 2025 at 4:16 PM
Nijar ta horas ta matasa don yaƙi da ƴan bindigar da suke tsallaka wa ƙasar daga Najeriya
Nijar ta horas ta matasa don yaƙi da ƴan bindigar da suke tsallaka wa ƙasar daga Najeriya
Kwararar ƴan bindiga daga Najeriya zuwa yankunan Madarunfa da Gidan Runji a Jihar Maradi da ke Jamhuriyar Nijar, ya sa hukumomin wannan yanki ɗaukar Matasa 300 aikin soja da nufin taimaka wa Jami'an tsaro tabbatar da zaman lafiya.
www.rfi.fr
November 11, 2025 at 9:18 AM